Thursday, May 1, 2008

Fatawa akan Azumi

TAMBAYA : Hadisin dayake cewa “ Kada kuyi Azumi ranar Asabar Face abinda aka Farlanta maku – wato Ramadan –“ shin Hadisin Ingantacce ne, kuma menene ma’anar Hadisin kuma shin ya kunshi dukkan Azumi ne?

ME BADA AMSA: Shaikh Abdur rahman bin Jibrin Mamba a cikin Majalisar manyan malamai masu fatawa a kasar Saudi Arabia.

AMSA: an kebance ranar Asabar ne da Hani saboda yahudawa sun kasance suna barin aiki a cikinta, se aka hana girmama ranar saboda kada ayi kamance – ceniya dasu, kuma ya halarta a Azumce Asabar idan akwai sababi, Kaman wanda yake Azumi rana ya sha ruwa rana, haka idan yayi dai- dai da ranar Arafa, ko Ranar Ashura da makamantansu, Ma’anar (abinda aka Farlanta maku) ma’anarsa aka shar’anta, kuma aka sunnanta maku.

No comments: