Wednesday, November 21, 2007

ABUBUWAN DA'AKA HALASTA MA ME AZUMI

ABUBUWAN DA'AKA HALASTA MA ME AZUMI SUNE KAMAR HAKA:


1. Shiga cikin Ruwa da yin nitso aciki da sanyaya jiki saboda tsananin zafi, Domin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance : ( "Yana zuba ruwa akansa, yana me Azumi saboda k�ishi ko saboda Zafi" Ahmad da Abu Dawud).

2. Yawayi gari yana me janaba ya halasta, Saboda fadin Nana A'isha Allah ya kara mata yarda :

( "Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yana wayan gari da janba yana Azumi sannan yayi wanka " Bukhari da muslim). wato acikin Azumin Ramadan.

3. Ci da Sha da Jima�i cikin dare har zuwa lakacin fitowar alfijir, Saboda fadin Ma�aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: ("Lallai Bilal yana kiran Sallah da dare, to kuci ku sha har se dan umm maktum ya kira sallah " Bukhari da muslim). Wato bilal nayin kira na farko shikuma yanayin kira na biyu.

4. Me jinin Haila da me jinin Bik'i, idan jinin ya yanke mata cikin dare ya halasta su jinkirta wankan har zuwa Asubahi, kuma su wayi gari da Azuminsu sannan suyi wanka kafin suyi Sallah.

5. Cin Aswaki a farkon Yini da karshensa, saboda cin Aswaki mustabbine kuma babu wani dalili da yanuna cewa za�ayi shi a wani lokaci banda wani, wannan shine mazhabin mafi yawan malamai.

6. Yin tafiya dan wata bukata ta halas koda tafiyan zatasahi shan ruwa.

7. Yin magani kowani Irii idan matukar baze tafi cikinsa ba kamar yin alluran da bata abinci bace.

8. Tauna abinci da d'and'ana shi da sharadin babu abinda zewuce ciki.

9. Yin amfani da turare da Shakan kanshi me dad'i.

Tuesday, November 20, 2007

KWANAKIN DA AZUMI YAKE HARAMUN A CIKINSU

KWANAKIN DA’AKA HARAMTA YIN AZUMI CIKINSU

1. Ranakun Idi guda biyu, Idi babba da Idi Krama, Saboda Fadin Umar dan khattab Allah yakara masa yarda: (“Lallai wadannan kwanaki guda biyu manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: yahana Azumi a cikinsu, Ranar da kuke shan daga Azuminku, da ranar da kuke ci daga yankanku” Muslim).
2. Kwanaki uku na shanyan nama (Ayyamut-tashreeq) wato kwanakin babban sallah guda uku, Sha daya da sha biyu da sha uku ga watan zulhijjah, Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: ya aiki Abdullahi dan Huzafah Allah yakara masa yarda yana kewayawa a muna yana cewa: (“kada kuyi Azumin wadannan kwanakin, domin su ranaku ne na cin da sha da ambaton Allah madaukakin sarki” Ahmad). Amma wannan banda mahajjaci, meyin tamattu’i da meyin Qiraani idan beda Hadaya.
3. Ranakun da mace take Haila da Bik’i, Saboda fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: a gameda hakkin mace, yace: (“Ba idan tayi haila bata sallah ba? To wannan shine tawaya -rashin cikan- addininta” Bukhari). Kuma malamai sunyi Ijma’i wato basuyi sabani ba akan bacin Azumin me haila da me bik’i.
4. Azumin mace idan mijinta na gari se idan ta nemi Izininsa, Saboda Fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: ( "Kada mace tayi Azumi alhali mijinta yana nan se dai idan da Izininsa amma banda Azumin ramadan" Bukhari da muslim).

RANAKUN DA'AKA HANA YIN AZUMI A CIKINSU

RANAKUN DA AKA KYAMACI YIN AZUMI CIKINSU (KARHANCI)

1. Yin Azumin Ranar Arafa ga mahajjaci wanda yake tsayuwan Arafa, Saboda Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: (“ Ranar Arafa da Ranar yanka –wato layya-, da kwanakin Shanya nama –wato kwanakin idi uku- Idinmu ne mu musulmai, kuma su kwanakin ci ne da sha” Abu dawud Tirmidhi).
2. Yin Azumin Ranar juma’a ita kad’ai, Saboda Fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: (“ kada kuyi Azumin ranar juma’ah ita kadai, sedai kafinta da rana daya ko bayanta da rana daya” Bukhari da muslim).
3. Yin Azumin Ranar Asabar ita kadai, Saboda Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: ( “kada kuyi Azumi ranar Asabar, se wanda aka wajabta maku ,idan da d’aya daga cikinku besami komaiba se bawon Inabi ko itacen bishiya to ya tattaunashi” Ahmad da Abu Dawud).
4. Azumin Shekara: Shine mutum yayi Azumin Shekara gaba daya ba tare da shan ruwa ba , Saboda Fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: (“Babu Azumi ga wanda yayi Azumin shekara” Bukhari da muslim). da Fadansa:
5. Zarcewa da Azumi kwana biyu a jere ko fiye da haka da gangan batare da ya sha ruwa ba, shine abinda ake kira da wisaali, Saboda Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: (“Ina kashedin ku dayin wisali” Bukhari da muslim). Da fadansa: (“Kada ku zarce –wato dayin Azumi- duk wanda yakeso yazarce, cikinku to ya zarce zuwa lokacin Sahur” Bukhari).
6. Azumin Ranar shakka, itace ranar talatin ga watan sha’aban saboda Fadin Ammar bin Yasir Allah yakara masa yarda: (“Duk wanda yayi Azumin ranar da ake shakka to hakika ya sabama Abul-qasim, Sallallahu Alaihi Wasallam” Abu Dawud da Tirmidhi). Kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yace: (“kada kurigayi ramadana da Azumin kwana daya k kwana biyu in banda mutumin da yakasance yanayin wani Azumi to se ya Azumceshi” Muslim).

Azumin Neman Lada (wato Nafila)

AZUMIN NEMAN LADA (NAFILA)

Manzan Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya kwadaitar da yin wadannan Azumin kamar haka:

1. Azumin kwana shida na watan Shawwal –watan salla karama- Saboda fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: ( “Duk wanda yayi Azumi Ramadan, sannan ya bisu da Azumi Shida na Shawwal..... za’a bashi lada kamar na wanda yayi shekara yana Azumi ba hutawa.
2. Azumin Ranakun Litin da Alhamis, dan Fadin Abu Hurairah Allah yakara masa yarda yace: (manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yafi yawan yin Azumi a Litinin da Alhamis, se akace masa wato aka tambayeshi dalilan dayasa yake Azumtansu, se yace: (“Ana bijiro da ayyuka akowace ranar litinin da Alhamis, se Allah ya gafartama kowani musulmi ko kowani mumini in banda masu gaba da juna, se yace: kujinkirta masu” Ahmad).
3. Azumin kwana uku a cikin kowani wata, Saboda fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: ( “Yin Azumin kwana uku a cikin kowani wata: Azumin Shekara, sune kwanakin biidh safiyan Sha uku, sha hudu,sha biyar” Nasa’i ).
4. Azumin ranakun farko na watan zul-hijjah, Saboda fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: ( “babu wasu kwanakin da Allah madaukakin sarki yafison Ayyukan Alkhairi a cikinsu kaman wadannan kwanank-wato kwanakin zulhijjah- sukace ya manzan Allah koda Jihadi akan tafarkin Allah? Yace koda Jihadi akan tafarkin Allah in banda kawai mutumin daya fita da kansa da dukiyarsa, sannan bedawo da komai ba” Bukhari). Wato kudin sun kare kuma yayi shahada. Kuma ranar da tafisu duka itace ranar Arafah, wato ranar tara ga watan zulhijjah, ga wanda ba mahajjaci ba Saboda Fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: (“Yin Azumin ranar Arafa yana kankare zunubban shekaru biyu, wadda ta wuce da me zuwa” Muslim). amma k'ananan zunubai ake nufi a Hadisin, manayan laifuka kuwa sedai tuba ke kankaresu.
5. Azumin Watan Muharram, Saboda fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: yayinda aka tambayeshi: wani Azumine yafi falala bayan Ramadan? Yace: (“watan Allah dakuke kira muharram” Muslim).
6. Azumin Ranar Ashura, shine ranar goma ga wata, Saboda fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: (“ kuyi Azumin ranar Ashura, yana kankare Shekaran data gabata” Muslim). Kuma Mustahabbi ne ayi Azumin ranar tara ga wata hade da goma saboda sab’awa Yahudawa da Nasara, domin sanda akacewa Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam gameda Azumin Ashura cewa yayi: “Rana ce da Yahudawa da Nasra suke girmamata” Se yace: ( “Idan Allah ya kaimu shekara mezuwa zanyi Azumin tara” shekaran bata zoba anzan Allah ya rasu) Muslim.

Saturday, November 3, 2007

Azumin Tsofaffi

Azumin watan tsofaffi,wato Azumine da'ake yinsa cikin watan Sha'aban wato wata na takwas cikin watannin musulunci, to menene hukuncin yin wannan Azumi? kuma shin an kebanceshi ne da tsofaffi kadai banda yara ko matasa?