ABUBUWAN DA'AKA HALASTA MA ME AZUMI SUNE KAMAR HAKA:
1. Shiga cikin Ruwa da yin nitso aciki da sanyaya jiki saboda tsananin zafi, Domin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance : ( "Yana zuba ruwa akansa, yana me Azumi saboda k�ishi ko saboda Zafi" Ahmad da Abu Dawud).
2. Yawayi gari yana me janaba ya halasta, Saboda fadin Nana A'isha Allah ya kara mata yarda :
( "Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yana wayan gari da janba yana Azumi sannan yayi wanka " Bukhari da muslim). wato acikin Azumin Ramadan.
3. Ci da Sha da Jima�i cikin dare har zuwa lakacin fitowar alfijir, Saboda fadin Ma�aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: ("Lallai Bilal yana kiran Sallah da dare, to kuci ku sha har se dan umm maktum ya kira sallah " Bukhari da muslim). Wato bilal nayin kira na farko shikuma yanayin kira na biyu.
4. Me jinin Haila da me jinin Bik'i, idan jinin ya yanke mata cikin dare ya halasta su jinkirta wankan har zuwa Asubahi, kuma su wayi gari da Azuminsu sannan suyi wanka kafin suyi Sallah.
5. Cin Aswaki a farkon Yini da karshensa, saboda cin Aswaki mustabbine kuma babu wani dalili da yanuna cewa za�ayi shi a wani lokaci banda wani, wannan shine mazhabin mafi yawan malamai.
6. Yin tafiya dan wata bukata ta halas koda tafiyan zatasahi shan ruwa.
7. Yin magani kowani Irii idan matukar baze tafi cikinsa ba kamar yin alluran da bata abinci bace.
8. Tauna abinci da d'and'ana shi da sharadin babu abinda zewuce ciki.